Dakarun Libiya sun yi nasara a kan mayakan IS
May 18, 2016![Misrata Küstenwache](https://static.dw.com/image/18527185_800.webp)
Dakaru masu biyayya ga gwamnatin Libiya wadda ke samun tallafin kasashen duniya sun samu nasara kan mayakan kungiyar IS da ke ikirarin neman kafa daular Islama a garuruwa uku na yammacin birnin Misrata, abin da ya janyo tarnaki ga nasarori da tsagerun kungiyar IS suka samu a baya.
Yanzu haka dakaraun gwamnatin na fafatawa da tsagerun na IS a wani waje da ke da nisan kilo-mita 50 daga birnin Sirte da ke zama tungar kungiyar. A wannan Laraba kungiyar kare hakkin dan Adam ta Human Rights Watch ta zargi 'yan kungiyar ta IS da aikata laifukan yaki inda take kashe fararen hula a birnin na Sirte.
Kasar ta Libiya da ke yankin arewacin Afirka ta tsunduma cikin rikicin tun shekara ta 2011, bayan juyin-juya halin da ya kawo karshen gwamnatin Marigayi Mu'ammar Gaddafi ta fiye da shekaru 40. Lamura sun kara dagulewa lokacin da aka samu gwamnatoci biyu masu adawa da juna a tsakiyar shekara ta 2014.