1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Dakarun RSF a Sudan amince da kudurin sulhu

Binta Aliyu Zurmi
November 7, 2025

Dakarun RSF a Sudan sun amince da shirin samar da ayyukan jin kai da kasashe Amurka da Masar da Hadaddiyar Daular Larabawa da Saudiyya suka kulla.

Kombobild Abdul Fattah Al-Burhan und Mohamed Hamdan Dagalo
Hoto: Bandar Algaloud/Mahmoud Hjaj/AA/picture alliance

Sanarwar ta biyo bayan kwace muhimmin garin El-Fasher da dakarun na RSF suka yi, wanda ya kori sojojin gwamnati daga tungarsu ta karshe a yammacin Darfur. 

Tuni dai ake zarginsu da aikata kisan kiyashi da sace-sace da cin zarafin mata bayan karbe ikon da garin, kazalika a kwanakin baya-bayan nan an ga yadda suka karkata zuwa yankin Kordofan da ke makwabtaka da su, inda ake ci gaba da gwabza kazamin fada. 

Gwamnatin da ke samun goyon bayan soji ba ta ce uffan ba game da sanarwar ta RSF. Tun a ranar Larabar da ta gabata, babban hafsan sojin Sudan Abdel Fattah al-Burhan ya ce dakarunsa na ci gaba da fafutukar fatattakar abokan gaba.

Sama da shekaru biyu aka kwashe ana gwabza kazamin yaki a Sudan wanda ya samo asali daga rikicin shugabanci ya hallaka  mutane da dama tare da raba dubbai da matsugunnensu.

Karin Bayani:Amurka ta kudiri aniyar kawo karshen yakin Sudan