An sako dalibai 28 a Kaduna
July 25, 2021![Nigeria Kaduna | Entführung Schüler Bethel Baptist School](https://static.dw.com/image/58168343_800.webp)
Talla
Rev. Israel Akanji shugaban Baptist Convention, ya ce fiye da sauran yara 80 har yanzu suna hannun masu garkuwa da jama'a, ya zuwa yanzu babu tabbacin lokacin da za a sake sauran yaran da ke tsare.
Sai dai 'yan bindigar sun bukaci kudin fansa har Naira 500,000 (kusan $ 1,200) ga kowane dalibi, amma makarantar ta ce ba ta biya ko sisi ba, sai dai kuma ba ta hana iyayen daliban daukar mataki ba.