1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW
Salon rayuwaNijar

Taron masu lalurar gani a Damagaram

November 11, 2025

A daidai lokacin kakar amfanin gona, masu lalurar gani yankin Afirka ta Yamma na gudanar da taronsu na shekara-shekara a yankin Damagaram na Jamhuriyar Nijar.

Jamhuriyar Nijar | Damagaram | Taro | Masu Lalurar Gani | Dalibai
Akwai dai korafi na karancin kayan karatu, ga daliban da ke da lalurar ganiHoto: DW/S. Boukari

Taron masu lalurar ganin na bana ya gudana ne, a daidai lokacin da galibin  al'ummar kasashen  nahiyar ke cikin yanayi na tabarbarewar tsaro. Sarkin makafin Damagaram Lawali Bahago ne, ya kasance mai masaukin baki. Bayan adu'o'i da wasanin kade-kade da bushe-bushe, sun kuma mika gaisuwa ga mai alfarma sultan na Damagaram kamar yadda suka saba. A yanzu dai magabatan kasashen sun dauki matakin tafiya tare da masu lalurar ganin da ma sauran masu bukata ta musamman, a kokarinsu na ganin an gudu tare an kuma tsira tare.

Najeriya: Mai lalurar gani da ke yin kitso

01:56

This browser does not support the video element.

Daga cikin mahalarta taro, har da sarkin makafin Sokoto da ke Tarayyar Najeriya Mahamadu Haruna. Gwamnan jahar Damagaram Kanal Sani Masallaci cewa ya yi: "Shugaban kasa Janar Abdourahamane Tiani da kuma duka manyan kasar nan sun ce in zo in mika gaisuwarsu.......Ba za ku sake ganin wani mai lalurar gani yana roko ko yana bara ba, za a sa niyya a gani ....a kawo musu agaji in ya so su samu abun yi........"

Tsallake zuwa bangare na gaba Bincika karin bayani