1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Burkina ta yi sabon shugaba

Zainab Mohammed Abubakar
February 16, 2022

An rantsar da Laftanar Kanar Paul-Henri Sandaogo Damiba a matsayin shugaban kasar Burkina Faso, makonni uku bayan hambarar da gwamnatin Roch Marc Kabore.

Burkina Faso | Militärleiter Paul-Henri Sandaogo Damiba
Hoto: Radiodiffusion TÈlÈvision du Burkina/AFP

A wani biki ta gidan talabijin na kasar ne dai, Damiba ya sha rantsuwar kama ragamar mulki tare da alkawarin kare martaba da darajawa kundin tsarin mulkin Burkina Faso.

An gayyaci 'yan jaridar cikin gida kalilan banda na ketare, a bukin da ya gudana a wani karamin daki a bainar wakilan majalisar tsarin mulkin kasar, majalisar da ta tabbatar da shi a matsayin shugaban kasa ahukumance a makon da ya gabata.

A ranar 24 ga watan Janairun ne dai Damiba, mai shekaru 41 da haihuwa ya jagoranci kifar da mulkin shugaba Kabore, biyo bayan fushin al'ummar kasar ta hanyar yin zanga zanga, kan yadda tsohon shugaban ke wa harkar tsaro rikon sakainar kashi, da ya jagoranci asarar rayuka.