1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Burkina Faso: Mayar da kasar hannun farar hula

January 28, 2022

Jagoran juyin mulkin sojin kasar Laftanat Kanal Paul-Henri Damiba ya bayyana a jawabinsa ga 'yan Burkina Faso cewa za a mayar da kasar kan tafarkin kundin tsarin mulkin kasa da zarar al'amura sun daidaita.

Burkina Faso I Col. Henri Sandaogo Damiba
Hoto: Sophie Garcia/AP/picture alliance

Damiba ya kuma ce bangarori daban-daban za su hadu don samar da jadawalin sauyi a gwamnatance, yayin da a 'yan kwanakin nan gwamnatin soji ta yi kokarin samun goyon bayan shugabannin addinai da ma na farar hula.

Yayin da yake jawabin daga fadar gwamnatin kasar cikin shigar sojoji, Laftanat Kanal Damiba ya ce matsalar tsaro ne babban batun da za a sa a gaba. A 'yan kwanakin nan ne dai dakarun soji suka hambarar da mulkin shugaba Roch Marc Kabore, bayan zarginsa da rashin yin katabus kan matsalolin 'yan tada kayar baya da kasar Burkina Fasi ke fuskanta.