1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW
SiyasaMexiko

Dan bindiga ya bude wuta a filin wasan kwallon kafa a Mexico

January 26, 2026

Hukumomin Mexico sun ce maharin ya kashe mutane 11, yayin da wasu 12 suka samu raunuka.

Yan sandan Mexico a cikin shirin ko-ta-kwana
Yan sandan Mexico a cikin shirin ko-ta-kwanaHoto: Rick Cruz/Zuma Press/picture alliance

Magajin Garin birnin Salamanca, Cesar Prieto, ya ce 'dan bindigar ya isa filin jim kadan bayan kammala wasan sada zumunci tsakanin matasa. Prieto ya ce lamarin na daya daga cikin kalubalen da ake fuskanta a Mexico, inda ya bukaci Shugaba Claudia Sheinbaum da ta yi duk mai yiwuwa wajen murkushe ayyukan 'yan bindiga a kasar.

Karin bayani:Mutum bakwai sun halaka a hadarin jirgin sama a Mexico

Mexico na daya daga cikin kasashen da ke fama da ayyukan kungiyoyin 'yan daba da masu ta'ammali da miyagun kwayoyi. Hukumomin Mexico sun ce an samu raguwar kashe-kashen mutane a 2025, idan aka kwatanta da 2016, wanda kashi 17.5 bisa 100 ke mutuwa a duk mutum 100,000.