1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Mali ta kara sulhu da 'yan tawaye

Abdoulaye Mamane Amadou
August 6, 2022

Shekaru bayan kasa tabbatar da yarjejeniyar zaman lafiya da 'yan tawaye, gwamnatin Mali za ta dauki tsoffin mayakan 'yan tawayen arewacin kasar aikin soja.

Mali Übergangspräsident Alioune Diop
Hoto: Annie Risemberg/AFP

Gwamnatin rikon kwarya ta mulkin soja a Mali ta cimma matsaya ta shimfida zaman lafiya da mayakan 'yan tawayen Abzinawa da ke arewacin kasar, inda za ta ba wa mutane dubu 26 daga cikin mayakan a guraben aiki.

Fadar mulki ta birnin Bamako ta ce za a dauki mutun dubu 13 a zangon farko na aiwatar da yarjejeniyar, kana bayan ba su horon sanin makamar aikin soja za su koma a yankunan arewacin kasar don kara tabbatar tsaro daga nan zuwa shekarar 2024.

A shekarar 2015 ce dai gwamnatin Mali ta kulla yarjejeniyar zaman lafiya a binrin Alger da 'yan awaren na Abzinawa masu ikrarin kafa kasar Azawak a arewacin Mali, sai dai an fuskanci tarnaki a gabanin fara aiki da yarjejeniyar bayan da aka kifar da gwamnatin farar hula a kasar watanni da dama da suka gabata.