An daure jagoran tsagerun Sudan
December 9, 2025
Kotun duniya mai hukunta manyan laifukan yaki da ke birnin Hague na kasar Netherlands ta yanke hukuncin daure shekaru 20 a gidan fursuna ga jagoran tsagerun kungiyar Janjaweed na Sudan, bisa laifukan yaki da aka yi kan al'ummar yankin Darfur a shekaru fiye da 20 da aka kwashe ana tarzoma.
Yanke hukuncin
Shi dai Ali Muhammad Ali Abd_Al-Rahman tun watan Oktoba aka same shi da laifuka 27 da aka tuhume shi.
Jagoran tsagerun Ali Abd_Al-Rahman ya taka muhimmiyar rawa a rikicin Darfur tsakanin shekara ta 2003 zuwa 2004 lokacin da mayakan suka aikata laifukan yaki kan dan Adam. Masu gabatar da kara a kotun ta duniya sun bukaci daure jagoran tsagerun na tsawon rai da rai, ganin irin rawar da ya taka a rikicin na Darfur da ke yammacin kasar Sudan.
A shekara ta 2005 Kwamitin Sulhu na Majaisar Dinkin Duniya ya bukaci kotun duniya mai hukunta laifukan yaki ta gudanar da bincike domin hukunta masu hannu bisa laifukan yaki a rikicin na Lardin Darfur da ke Sudan.