1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Turkiyya: Kotu ta yanke hukunci kaso ga Bajamusa

Gazali Abdou Tasawa
November 14, 2018

Wata kotun kasar Turkiyya ta yanke hukuncin dauri na shekaru shida ga wata Bajamusa bayan samun ta da laifin mu'amala da Kungiyar 'yan ta'adda.

Türkei Gericht in Silivri
Hoto: picture-alliance/AP Photo/L. Pitarakis

A kasar Turkiyya, wata kotun birnin Edirne na Arewa maso yammacin kasar ta yanke a wannan Laraba hukuncin zaman kaso na tsawon shekaru shida da watanni uku ga wata mata Bajamusa mawakiyar Kurdawa da ke da zama a birnin Kolon a bisa samunta da laifin kasancewa mamba ga kungiyar ta'adda. 

A ranar 23 ga watan Yunin da ya gabata ne dai mahukuntan Turkiyyar suka kama matar mai suna Saide Inac da aka fi sani da Hozan Cane a daidai lokacin da take rakkiyar jam'iyyar HDP mai kusanci da jam'iyyar PKK ta Kurdawa a lokacin yakin zaben shugaban kasa da na 'yan majalisar dokoki da Turkiyyar ta shirya a ranar 24 ga watan Yuni da ya gabata. 

Sai dai lauyenta Mustafa Peköz ya ce zai daukaka kara. Yanke wa wannan Bajamusa hukuci na zuwa ne a daidai lokacin da kasashen Turkiyya da Jamus suka soma kyautata dangantakarsu wacce ta fuskanci komabaya a watannin da suka gabata.