1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Dbeibah da Bachagha: Wa ke mulkar LIbiya?

Mouhamadou Awal Balarabe
March 1, 2022

Majalisar dokokin Libiya ta amince da sabuwar gwamnati da Fathi Bachagha ke jagoranta, tare da bijire wa ta Abdelhamid Dbeibah da ke birnin Tripoli bayan da ta ki mika mulki cikin ruwan sanyi.

Die zwei libyschen Führer Abdul Hamid Dbeibah und Fathi Bashagha
Hoto: picture-alliance

'Yan majalisa 92 ne suka kada kuri'ar amincewa da gwamnatin Fathi Bashagha daga cikin 101 da suka halarcin zaman a birnin Tobruk da ke gabashin kasar. Sai dai wannan matakin zai iya sake jefa Libiya cikin rikicin shugabancin tsakanin bangarori da ke gaba da juna, kamar yadda ta kasance tsakanin a shekarun baya.

Idan za a iya tunawa, a  ranar 10 ga Fabrairu ne, majalisar ta Libiya ta nada Bachagha domin ya maye gurbin Dbeibah a matsayin shugaban gwamnatin wucin gadi. Sai dai firaminista da ke ci ya ce ba zai mika mulki ba matakiar da zababbiyar gwamnati ba ce. Ire-iren wadannan rigingimun siyasa sun sa a dage zabe sau biyu a Libiya, duk da fatan da kasashen duniya ke yi na kawo karshen rudanin da ya addabi kasar.