Dokar hana fita a Liberia don yaƙi da Ebola
August 20, 2014Talla
Gwamnati ta ƙaddamar da dokar hana fitan daren a faɗin ƙasar, bisa matakan shawo kan bazuwar cutar ta Ebola. An kuma killace wasu anguwanni biyu cikin birnin Monrovia, inda wasu da ake jinya tun da farko suka tsere kafin a ganosu.
A halin da ake ciki Majalisar Ɗinkin Duniya na yin wani yuƙurin ganin ƙwararru masu kula da sha'anin kiwon lafiyar sun samu nasarar shawo kan bazuwar cutar ta Ebola a yammacin Afirka.
Mawallafi: Usman Shehu Usman Edita: Abdourahamane Hassane