1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW
SiyasaAfirka

Doumbouya da ya yi juyin mulki a Guinea ya lashe zabe

December 31, 2025

Shugaban Gwamnatin Mulkin Sojin Guinea Mamady Doumbouya ya lashe zabe da gagarumar rinjaye, bayan murkushe 'yan hamayya ko kuma tilasta musu hijira.

Mamady Doumbouya da matarsa
Mamady Doumbouya da matarsaHoto: Kommunikationsdienst der Präsidentschaft von Guinea

Hukumar zaben kasar ta bayyana Doumbouya a matsayin wanda ya samu nasara da kashi 86.71 bisa 100 na yawan kuri'un da aka kada. Doumbouya wanda ya kwace ragamar shugabancin kasar ta hanyar juyin mulki a 2021, bayan hambarar da gwamnatin Alpha Conde, ya rikide zuwa farar hula domin ci gaba da jan ragamar kasar a wani salo na dimukuradiyya mai kama da kama karya. Dama dai an yi hasashen cewa shi ne zai lashe zaben ba tare da hamayya ba.

Karin bayani:Al'ummar Guinea sun fara kada kuri'ar zaben shugaban kasa

Gabanin gudanar da zaben shugaban kasar na Guinea, an haramta wa ‘yan adawa da dama tsayawa takara, a yayin da wasu suka tsere zuwa kasashen ketare domin neman mafakar siyasa. Sannan gamayyar shugabannin jam'iyyun adawa sun bukaci daukacin al'umma da su kauracewa zaben.

Tsohon minista a gwamnatin Guinea, Yero Balde, Shi ne ya zo na biyu a zaben, inda ya samu kashi 6.51 bisa 100 na yawan kuri'un da aka kada.

.