1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Dubbai na cikin mawuyacin hali a yankin Afar na Habasha

February 8, 2022

Sama da shekara guda da rikicin yankin Tigray na Habasha da ma ayyana dakatar da kai hare-hare, dubban jama'a na ci gaba da fama da matsaloli a yankin Afar.

Äthiopien l Geflüchtete Menschen in Afar Iwa
Hoto: Seyoum Getu/DW

Gwamnatin yankin Afar da ke Habasha, ta ce sama da mutum dubu 300 ne suka rasa muhallansu daga watan Disambar bara zuwa yanzu, tana mai dora laifi a kan mayakan yankin Tigray.

Baya ga wannan zargi na daidaita mutane a yankin, hukumomin na Afar sun ce mayakan na Tigray sun kakkashe mutane tare da sace dukiyoyi masu yawa a yankin.

Ita ma Majalisar Dinkin Duniya ta ce rikici a yankin na Afar, ya hana ta damar kai kayayyakin jin kai ga dubban mabukata da ke a a yankuna masu makwabtaka da Tigray da matsalar fari ta shafa.

Cikin watan Nuwambar 2020 ne dai fada ya barke tsakanin gwmanatin Habasha da kawayenta ciki har da wadanda ke a yankin na Afar, da kuma mayaka masu fafutikar kare al'umar Tigray.