1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Dusar kankara ta halaka mutane 61 a Afghanistan

January 24, 2026

Rahotanni daga birnin Kabul na Afghanistan na cewa dusar kankara da ruwan sama mai karfi ya halaka mutane akalla 61 a cikin kwanaki uku.

Afghanistan | Schneefall in Kabul
Hoto: Wakil KOHSAR/AFP

Mai magana da yawun Hukumar Bada Agajin Gaggawa, Mr. Parwan shi ne ya tabbatar da hakan kamar yadda ya wallafa a shafin X, ya ce mutane kimani 110 sun samu raunuka, yayin da wasu kimanin 450 suka rasa muhallansu. A jamlace dai dusar kankarar ta shafi mutane kimanin 360.

Hukumomin lardin Bamyan na ci gaba da aike wa da kayan abinci ga mutanen da suka makale a kankara, tare da gargadin mutane da su kaucewa bin titunan da dusar kankarar ta mamaye.