1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW
SiyasaAsiya

Duterte ya isa kasar Netherlands don fuskantar shari'a a ICC

Mouhamadou Awal Balarabe
March 12, 2025

Kotun Hukunta Manyan Laifuka ta Duniya ICC ta ce akwai kwararran shaidu da ke nuna cewar tsohon shugaban Phillipines Rodrigo Duterte ya aikata laifin cin zarafin bil'adama da aikata kisan kai a lokacin yakin neman zabe.

Tsohon shugaban Philippines Rodrigo Duterte kafin a kai shi kotun ICC
Tsohon shugaban Philippines Rodrigo Duterte kafin a kai shi kotun ICCHoto: Veronica Duterte via Instagram/REUTERS

Kotun hukunta manyan laifuka ta duniya ta tabbatar da isowar jirgin sama da ke dauke da tsohon shugaban Phillipines Rodrigo Duterte a kasar Netherlands, domin fuskantar shari'a bisa zarginsa da aikata laifuffukan yaki da safarar miyagun kwayoyi. Kakakin kotun ICC Fadi El Abdallah ne ya ba da wannan tabbaci ga manema labarai a birnin The Hague, inda ya ce  za a fara kai Duterte gidan yari kafin a gurfanar da shi a gaban kotu a cikin kwanaki masu zuwa.

Mista Duterte, mai shekaru 79, ya kasance tsohon shugaban kasar nahiyar Asiya na farko da za a gurfanar a gaban kotun ICC, wacce ta ce akwai kwararran shaidu da ke nuna cewar ya aikata laifin cin zarafin bil'adama da aikata kisan kai a lokacin yakin neman zabe. Sai dai, duk da cewa Philippines ta fice daga ICC a 2019, amma kotun na ci gaba da hukumta kashe-kashen da suka faru kafin janyewar, da kuma wadanda aka aikata a birnin Davao lokacin da Rodrigo Duterte ya kasance magajin gari.

 

Tsallake zuwa bangare na gaba Babban labarin DW

Babban labarin DW

Tsallake zuwa bangare na gaba Karin labarai daga DW