1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW
Lafiya

Ebola ta sake ta'azzara a Congo

July 31, 2026

Mahukuntan kiwon lafiya a Jamhuriyar Dimokuradiyyar Congo sun ce adadin masu kamuwa da cutar Ebola ya haura 3,500 a larduna biyar na kasar.

Shugaban Congo Félix Tshisekedi
Shugaban Congo Félix Tshisekedi Hoto: Andrew Caballero-Reynolds/AFP

Adadin ya zarce yawan wadanda suka kamu a annobar da ta fi muni tsakanin shekarun 2018 da 2020.

Alkaluma sun nuna cewa mutane 1,556sun mutu kawo yanzu, yayin da annobar ke ci gaba da yaduwa musamman a lardin Ituri da ke gabashin kasar, yankin da ya dade yana fama da rikice-rikice.

Karin bayani : Ya za a shawo kan matsalar Ebola a Kwango?

Hukumar Lafiya ta Duniya ta ce har yanzu babu ingantacciyar allurar rigakafi ko maganin nau'in cutar Ebolan da ya bulla a Congo, sai dai ana ci gaba da gwaje-gwajen sabbin alluran rigakafi domin dakile yaduwarta.

Tsallake zuwa bangare na gaba Babban labarin DW

Babban labarin DW

Tsallake zuwa bangare na gaba Karin labarai daga DW