ECOWAS/CEDEAO ta cika shekaru 50 da kafuwa
May 28, 2025
Kungiyar ta ECOWAS/CEDEOA tana bikin lokacin ta kasashen yankin na yammacin Afirka suke cikin kalubale kan kudin fito na kayayyakin da ake kai wa zuwa kasar Amurka da kuma janye tallafin kasashen duniya da gwamnatin kasar ta yi. Kana kasashe uku na kungiyar Mali, Burkina Faso da Jamhuriyar Nijar da sojoji suka kwace madafun iko sun fice daga cikin kungiyar a farkon wannan shekara.
Karin Bayani: Wakilan Kungiyar AES na tattaunawa kan manufofin kungiyar
Kasashen da ke cikin kungiyar ECOWAS suna fama da kalubalen tsaro na kungiyoyin masu ikirarin jihadi. Kasashen Najeriya da Jamhuriyar Benin sun fuskanci hare-haren tsageru masu kaifin kishin addinin Islama cikin wtaannin da suka gabata. Kana juye-juyen mulkin soja irin wanda aka gani a kasashen uku (Mali, Burkina Faso da Jamhuriyar Nijar) da suka fice daga cikin kungiyar.
Daga cikin shugabannin kasashen na ECOWAS da suka saka hannu wajen kafa kungiyar shekaru 50 da suka gabata, tsohon shugaban gwamnatin mulkin sojan Najeriya Janar Yakubu Gowon mai ritaya ne kadai ya rage a raye, wanda yake da shekaru 90 da haihuwa.