Shirin ECOWAS na daukar matakan soja
August 4, 2023![Najeriya | Abuja | ECOWAS | CEDEAO | Taro | Nijar | Juyin Mulki](https://static.dw.com/image/66424636_800.webp)
Talla
Shugabannin sojojin kasashen Afirka ta Yamma sun sanar da hakan ne, jim kadan bayan kammala wani taro da suka yi a Abuja fadar gwamnatin Najeriya. Kwamishinan harkokin siyasa da zaman lafiya da tsaro na kungiyar Habaka Tattalin Arzikin Kasashen Yankin Afirka ta Yamman Abdel-Fatau Musah ne ya bayyana hakan, yana mai cewa za su dauki wannan mataki in har sojojin da suka kifar da gwamnati a Nijar din ba su sauka daga kan kujerar nakin da suka hau ba.