ECOWAS za ta yi taro kan Nijar
July 28, 2023![Nigeria | ECOWAS Gipfel](https://static.dw.com/image/60100588_800.webp)
Talla
Fadar shugaban Najeriya wanda shi ne ke jagorantar kungiyar ta ECOWAS ita ce ta sanar da haka. Kungiyar ta ECOWAS ta na shirin daukar mataki a kan nijar din. A karon farko tun bayan juyin mulkin da ya yi sabon jagoran mulkin sojin na Nijar Janar Abdourahamane Tchiani ya yi jawabi a gidan telbijan da rediyo na kasar inda ya bayyana dalilansu na yin juyin mulki.