Ecowas za ta tattauna batun Nijar
December 10, 2023![](https://static.dw.com/image/66408770_800.webp)
Talla
Yau aka shirya shugabannidaga kungiyar raya tattalin Arzikin Kasashen yankin yammacin Afrika wato ECOWAS za su gudanar da wani taro a Abuja babban birnin Najeriya. Ana sa ran taron zai tattauna batutuwan da suka shafi juyin mulkin da sojoji suka yi a Nijar da yunkurin kwace mulki a Saliyo da Guinea Bissau.Kungiyar ta ECOWAS ta sakawa Nijar takunkunmi karya tattalin arziki bayan da sojoji suka kifar da gwamnatin fara hula ta Bazoum Mohmed a cikin watan Yulin da ya gabata.