EU za ta saka wa Iran sabbin takunkumai
January 23, 2023![Flagge Iran und EU](https://static.dw.com/image/62808503_800.webp)
Talla
Jami'an diflomasiyyar EU sun ce kusan mutum 40 da kamfanoni da kungiyoyi ne wannan sabbin takunkuman za su shafa bisa take hakkinn al'umma da suka ce ana yi a kasar ta Iran.
Tun a watan Satumba bayan zanga-zangar da ta barke a kan mutuwar matashiya Mahsa Amini a hannun jami'an gyara hali na Hisba, Tehran ke amfani da karfi ta na murkushe masu boren. A baya-bayan nan ma ta rataye sama da masu boren 4.
Ko baya ga wadannan takunkuman, ministocin na tafka muhawarar ayyana jami'an hisba Iran a matsayin 'yan ta'adda.