EU na son wanzar da zaman lafiya a Libya
March 16, 2015Talla
A wani taro da suka yi dazu a birnin Brussels na kasar, ministocin suka ce ba za su yi kasa a gwiwa ba wajen dafawa kasar ta Libya don komawa kan duga-duganta muddin ta samu gwamnatin hadin kan kasa da kowa zai amince da ita a Libya din.
Tuni dai ministocin suka ce sun umarci babbar jami'ar harkokin wajen kungiyar da ta bada shawarwari kan tsare-tsare na yadda za a girka rundunar da za ta hada dakaru daga kasashen kungiyar kwatankwacin wadda ta yi aiki a Jamhuriyar Afirka ta Tsakiya don tallafawa Libya din ta samu zaman lafiya.