Tarayyar Turai na tattaunawa da Taliban a Brussels
June 23, 2026
Gwamnatin Belgium ta bai wa jami'an Taliban bizar wucin gadi domin halartar taron. Matakin na daya daga cikin manyan matakan inganta hulda tsakanin kungiyar EU da gwamnatin Taliban tun bayan da kungiyar ta karbi mulki a Afghanistan a shekarar 2021.
Tattaunawar na mayar da hankali ne kan batutuwan kaura da yadda za a mayar da wadanda ba su cancanci ci gaba da zama a Turai ba, lamarin da ke ci gaba da haifar da muhawara kan dangantaka da gwamnatin Taliban da kuma kare hakkin dan Adam a kasar Afghanistan.
Gwamnatocin kasashen Turai na kara matsa kaimi wajen daukar tsauraran matakai kan bakin haure, yayin da batun ke ci gaba da daukar hankali ta fuskar siyasa a fadin nahiyar.
Alkaluma daga hukumomin EU, kasashe membobin kungiyar sun karbi kusan bukatun neman mafakar 'yan Afganistan miliyan daya tsakanin 2013 zuwa 2024, an kuma amince da kusan rabin adadin mutanen.
Kimanin kasashen EU 20 ne suka nuna sha'awar mayar da wasu 'yan kasar Afganistan wadanda ba su samu izinin zama ba, musamman wadanda aka samu da aikata manyan laifuka ko kuma wadanda aka yi la'akari da barazanar tsaro a tattare da su.