1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

EU: Sabbin manufofi kan 'yan gudun hijira

Abdullahi Tanko Bala
May 14, 2024

Bayan tsawon shekaru ana tafka muhawara kungiyar tarayyar Turai za ta gabatar da sabbin dokoki kan 'yan gudun hijira da 'yan cirani tare da tsaurara tsaro a kan iyakokin kasashe mambobin EU

Tsaron kan iyaka tsakanin Girka da Turkiyya
Tsaron kan iyaka tsakanin Girka da TurkiyyaHoto: Nicolas Economou/NurPhoto/picture alliance

Ministocin tattalin arziki daga kasashe 27 na kungiyar tarayyar Turai sun amince da bukatar yin garanbawul ga manufofin kungiyar kan 'yan gudun hijira da masu neman mafaka.

Shirin ya bukaci tsaurara matakai a kan iyakoki da kuma raba hidimar daukar nauyin masu neman mafaka a tsakanin mambobin kasashen Turan.

Garanbawul din da zai kunshi gyaran sassan dokoki guda goma ya sami amincewar galibin kasashen kungiyar ta EU duk da turjiyar da kasashen Hungary da Poland suka nuna.

Sabbin dokokin za su fara aiki ne daga shekarar 2026.