EU za ta taimaka wa Afirka magance tsaro
February 27, 2020Talla
Shugabar hukumar tarayyar Turai Ursula Von der Layen ta yi alkawarin taimakawa kungiyar tarayyar Afirka magance rikice rikice a nahiyar da suka hada da rikicin kasar Libya.
Von der Layen ta baiyana ta baiyana hakan ne a yau Alhamis yayin ziyarar da ta kai hedikwatar kungiyar tarayyar Afirka a birnin Addis Ababa na kasar Habasha.
Ta ce kasancewar tarayyar Turai na tare da kungiyar hadin kan Afirka abu ne mai muhimmanci wajen wanzar da cigaba a nahiyar.
Kokarin kawo karshen rikicin Libya misali ne na kyakkyawar dangantakar da ke tsakanin kungiyar tarayyar Turai da kungiyar hadin kan Afirka.