1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Fada tsakanin magoya baya da masu adawa da Assad ya jawo rasa rayuka

March 21, 2014

Wani tashin hankali da ya auku tsakanin masu goyon bayan shugaban Siriya da wadanda ke adawa da shi a kasar Lebanon ya hallaka mutane 7 yayin da 11 suka jikkata.

Der syrische Präsident Bashar al-Assad während eines Interviews für AFP
Shugaban Siriya Bashar al-AssadHoto: AFP/Getty Images

A kalla mutane bakwai ne aka bada labarin rasuwarsu a wannan Juma'ar (21.03.2014) a birnin Tripoli da ke arewacin kasar Lebanon, bayan da fada ya barke tsakanin masu adawa da shugaban Siriya Bashar al-Assad da kuma magoya bayansa.

Masu aiko da rahotanni suka ce daga cikin wadanda suka rasa ransu har da wani dattijo, yayin da kimanin mutane 11 suka jikkata.

Dama dai an jima ana takun saka tsakanin mabiya tafarkin Sunnah na wannan gari na Tripoli da 'yan Alawiyya wanda ke goyon bayan Shugaba Assad, wanda yanzu haka ya ke fuskantar tada kayar baya a kasarsa daga masu rajin ganin ya kau daga mulki.

Mawallafi: Ahmed Salisu
Edita: Saleh Umar Saleh