1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Kogin Nilu: Kokarin sasanta rikici

June 27, 2020

Shugabannin kasashen Masar da Sudan da Habasha sun amince kowa ya dakatar da daukar mataki na gaba a kan kogin Nilu da suke takaddama a kai.

BG Grand Renaissance Dam | Der äthiopische Premierminister Abiy Ahmed Ali mit dem ägyptischen Präsident Abdel-Fattah al-Sisi (2018)
Hoto: Imago Images/Xinhua

Wata sanarwa da suka fitar a baya-bayan nan, na zaman babban mataki wanda ka iya yayyafa ruwa a kan  wutar da ta kunno kai tsakanin kasashen uku.

Rigama a kan Kogin na Nilu wanda ya ratsa kasashen uku, ta fara ruruwa tun kusan  shekaru 10 da suka wuce. Sai dai yunkurin Habasha na datse wani bangare na kogin don aiwatar da shirinta na samar da hasken wutar lantarki ga kasarta ya samu turjiya, inda Sudan da Masar suka nuna cewa ta wannan kogi ne suke samun ruwan sha.

Kasashen Sudan da Masar din dai sun bayyana cimma wata yarjejeniya a ranar Jumma'ar da ta gabata, biyo bayan wani taro da suka yi a karkashin kungiyar Tarayyar Afirka AU,  da shugaban Afirka ta Kudu Cyril Ramaphosa ya jagoranta.