SiyasaAfirka
Faransa ta fara janye jami'an diflomasiyyarta daga Mali
November 21, 2025
Talla
Faransa na shirin rage jami'an diflomasiyyarta na kasar Mali, sanadiyyar tabarbarewar tsaro da ke kara munana a kasar daga kungiyoyi masu ikirarin jihadi.
Ma'aikatar harkokin wajen Faransa ta ce yawaitar hare-haren ta'addanci sun janyo zaman dar-dar cikin tsoro da fargaba, a kasar ta yammacin Afirka, ko da yake za ta ci gaba bibiyar halin da ake ciki.
Karin bayani:Nijar: Matasan da ke zuwa Mali na komawa gida
Tuni dai kasashen irin su Amurka da Burtaniya suka fara kwashe wasu jami'an diflomasiyyarsu daga kasar, domin kare rayukansu daga hare-haren ta'addanci, wanda ke ci gaba da haddasa asarar rayukan jama'a ba adadi.