1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Sojojin Faransa sun halaka dan IS a Nijar

December 21, 2021

Sanarwar da sojojin Faransar suka fitar ta ce tun a shekara ta 2021 lokacin da IS ta kai wa Faransawa hari a Nijar aka tura wasu sojoji na musamman kan iyakar Nijar da Burkina Faso da Mali domin su gano 'yan ta'addar. 

Mali Französische Soldaten
Hoto: Daphné Benoit/AFP/Getty Images

Sojojin Faransa sun sanar a wannan Talata cewa sun yi nasarar kashe daya daga cikin 'yan ta'addar IS da suka kai wa ma'aikatan agaji na Faransa da ke aiki a Jamhuriyar Nijar hari a shekarar da ta gabata. 


Faransawan sun ce a ranar Litinin ne dai sojojin nasu hadin gwiwa da na Nijar suka bindige dan ta'addar a wani hari ta sama bayan da aka samu labarin cewa yana cikin wadanda suka halaka Faransawa a bara.


'Yan kungiyar ta IS dai sun halaka Faransawa shida da wasu 'yan Nijar biyu a lokacin da suka kai hari kan ma'aikatan agajin na Faransa a shekarar da ta wuce. A watan Agustar da ya gabata sojojin Faransan sun ce sun bindige jagoran mayakan IS da suka kitsa harin.
 

Tsallake zuwa bangare na gaba Babban labarin DW

Babban labarin DW

Tsallake zuwa bangare na gaba Karin labarai daga DW