Faransa ta nesanta kanta da rikicin Libiya
January 5, 2015![](https://static.dw.com/image/17312409_800.webp)
Talla
Shugaban na Faransa ya ce ya kyautu kasashen su yi abun da ya dace don ganin an samu tattaunawa tsakanin bangarorin, ta yadda za'a mayar da doka da oda a wannan kasa ta Libiya.
Shugaba Hollande na Faransa ya yi wadannan kalamai ne ta gidan radion kasar ta Faransa na France Inter. A baya-bayannan dai, kasashen d ke makwabtaka da kasar ta Libiya da suka hada da Nijar da Chadi, sun yi fatan ganin an dauki matakan soja kan kasar ta Libiya, wadda ake tsoron rikicin n ta zai ci gaba da shafar makwabtanta.