1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW
SiyasaAfirka

Zanga-zanga ta fadada a Najeriya duk da matakin gwamnati

Uwais Abubakar Idris SB
October 13, 2020

A Najeriya kashedin hatsarin takadamar da ake ci gaba da yi a tsakani  sifeto janar na rundunar ‘yan sandan kasar da hukumar kula da ayyukan ‘yan sanda a kan batun daukan sabbin ‘yan sandan da kotu ta dakatar.

Nigeria | Protest nach Vergewaltitung
Hoto: Kola Sulaimon/AFP/Getty Images

A Najeriya kungiyar kare hakkin jama'a ta CISLAC ta yi kashedin hatsarin da ke tattare da takadamar da ake ci gaba da yi a tsakani  sifeto janar na rundunar ‘yan sandan kasar da hukumar kula da aiyyukan ‘yan sanda a kan batun daukan sabbin ‘yan sandan da kotu ta dakatar a dai dai lokacin da ake ci gaba da fuskantar zanga-zanga ta neman yiwa daukacin aikin ‘yan sandan garambawul. Takadamar dai tsakanin sassan biyu da suke gudanar da harkokin ‘yan sandan a Najeriya da ta kai su ga shige da fice a kotunan kasar  ta kawo cikas a kan shirin daukan karin ‘yan sandan da ake matukar bukatarsu saboda kalubale na rashin tsaro a kasar.

Karin Bayani:  Najeriya: Murna bayan rusa rundunar SARS

Matakin baya-bayan nan kotu ta sake karbe ikon daukar sabbin ‘yan sandan daga hannun sifeto janar na Najeriya tare da mayar da shi ga hukumar kula da aikin ‘yan sandan, abin da ya dauki hankalin kungiyar ta CISLAC. Malam Auwal Musa Rafsanjani shine shugaban kungiyar ya bayyana abinda ke daga masu hankali. To sai dai ga Hajiya Naja'atu Bala Muhammad daya daga cikin mabobin hukumar kula da aiyyukan ‘yan sanda na bayyana yadda doka ta tsara lamarin.

Hoto: Adekunle Ajayi/NurPhoto/picture-alliance

A dai lokacin da ake ci gaba da fuskantar  zanga-zanga a Najeriya kungiyar datawan arewacin kasar ta bayyana bukatar lallai a yi wa daukacin tsarin hukumomin tsaro har da sauya manyan hafsoshin sojan kasar don kawo karshen kasha-kashen jama'ar da ake yi. Kungiyoyin kare hakkin jama'a dai na masu dagewar cewa dole ne a yi garambawul a kan daukacin aikin ‘yan sanda kamar yadda Mallam Auwal Musa Rafsanjani na kungiyar CISLAC ya bayyana. A bayyane yake a fili cewa Najeriyar na fuskantar kalubale mai yawa tun ma kafin batun rusa rundunar 'yan sanda da ke yaki da ‘yan fashi da ma matsin lamba na neman yi wa  daukacin tsarin tsaron kasar garambawul.

Tsallake zuwa bangare na gaba Bincika karin bayani