1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Sudan: Fargabar aikata laifukan yaki

Lateefa Mustapha Ja'afar
June 29, 2023

Mazauna birnin Khartoum fadar gwamnatin Sudan sun bayyana jin karar fashewar wani abu a shalkwatar sojojin kasar, a daidai lokacin da ake ci gaba da gwabza fada tsakanin sojojin da ke gaba da juna.

Sudan | Khartoum | Yaki
Hayaki na ci gaba da turnuke biranen SudanHoto: Stringer/IMAGESLIVE via ZUMA Press Wire/picture alliance

An dai ga hayaki ya turnuke yankin da shalkwatar sojojin take a tsakiyar birnin na Khartoum a yini na biyu na bukukuwan idin babbar salla, duk da sanarwar cimma yarjejeniyar tsagaita wuta da bangarorin biyu da ke yakar juna suka yi gabanin bukukuwan sallar. Wannan dai na zuwa ne a daidai lokacin da kungiyar bayar da agaji ta kasa da kasa ta Red Cross, ta sanar da shiga tsakani tare da tabbatar da cewa bangarorin biyu na gwamnati da kuma 'yan tawayen RSF sun amince da sakin firsinonin yaki a tsakaninsu. Tuni ma dai sojoji 125 da kungiyar ta RSF ta kama suka isa cikin iyalansu bayan ta sake su, sai dai kuma har kawo yanzu Majalisar Dinkin Duniya ta yi gargadin cewa hare-haren RSF din da na Larabawan yankin Darfur da ke mara musu baya ka iya haifar da aikata manyan laifuka kan dan Adam.