Côte d'Ivoire : Yiwuwar barkewar rikici a zaben
October 30, 2020![Elfenbeinküste Wahlen Alassane Ouattara](https://static.dw.com/image/54928757_800.webp)
Talla
Lamarin ya faru ne a kusa da garin Agbaou mai tazarar kilomita 150 da arewacin birnin Abidjan, kana wata majiyar tsaro ta shedawa kamfanin dillancin labaru na AFP da cewa ba wanda ya samu rauni a harin.
Ana dai ci gaba da gudanar da yakin neman zaben kasar a cikin wani yanayi na rudani da fargabar tashe-tashen hankula, inda kawo yanzu mutun 30 suka hallaka tun bayan yunkurin shugaban kasar na zarcewa karo na uku akan madafan iko.