1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Firaministan Faransa ya yi watsi da soke wasu ranakun hutu

Binta Aliyu Zurmi
September 14, 2025

Firaministan Faransa Sebastien Lecornu ya yi watsi da shirin tsohon firtaministan kasar na soke wasu ranakun hutu biyu da ya janyo takaddama.

Frankreich Paris 2025 | Sebastien Lecornu im Élysée-Palast nach Ernennung zum Premierminister
Hoto: Gao Jing/Xinhua/picture alliance

A wata hira da manema labarai firaministan ya ce akwai bukatar bijiro da wasu hanyoyin samar da kudaden shiga don farfado da komadar tattalin arzikin da kasar ke fuskanta.

Faransa dake zama kasa ta biyu mafi girma a tattalin arzikin yankin kasashe masu amfani da kudin Euro, yanzu ita ce kasa ta uku dake da dimbin bashi bayan kasashen Girka da Italiya.

Gibin kasafin kudin kasar na wannan shekarar ya kai kashi 5.8%, sama da kaso 3% na abin da kasashen EU suka amince.

A farkon makon nan ne majalisar dokokin Faransa ta kada kuri'ar yanke kauna ga Firaminista Francois Bayrou, watanni tara bayan ya dare kan madafun iko.

 

Karin Bayani:Faransa ta shiga wani wadi na tsaka mai wuya a siyasa