1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW
SiyasaAfirka

Ganawa tsakanin Masar da Turai

Suleiman Babayo ATB
October 22, 2025

Shugaban Masar Abdul Fattah el-Sisi ya nufi Brussels don tattaunawa kan yadda kungiyar EU za ta taimaka wajen sake bude mashigar Rafah, da kuma ba da karin taimako zuwa Gaza.

Masar | Shugaba Abdel-Fattah el-Sissi
Shugaba Abdel-Fattah el-Sissi na kasar MasarHoto: Evan Vucci/AP Photo/picture alliance

Ana ganawa ta farko tsakanin kasar Masar da kungiyar Tarayyar Turai inda shugabanni daga bangarorin biyu za su gana kan batutuwan tsaro da cinikayya gamida masu hijira, har da batun yankin zirin Gaza na Falasdinu.

Shugaba Abdel-Fattah el-Sissi na kasar ta Masar yana ganawar a birnin Brussels na Belgiyam tare da shugabar hukumar Tarayyar Turai, Ursula von der Leyen gami da shugaban gudanarwar hukumar António Costa. Akwai kuma batun yankin zirin Gaza na Falasdinu da aka smau yarjejeniyar tsagaita wuta tsakanin mayakan Hamas da gwamnatin Isra'ila.

Shugabar hukumar Tarayyar Turai, Ursula von der LeyenHoto: Yves Herman/REUTERS

Kungiyar Tarayyar Turai ta fi karkata ga Masar don samun gozon bayan cimma wannan aiki, sai dai kuma Turai ta dade tana sukar matakin Shugaba al-Sisi kann ctake hakkin bil Adama tun bayan abin da suka kira kwace mulki da karfi a 2013. Paul Taylor babban jami’i ne na cibiyar tsara manufofin EU.

Ana sa ran ganawar da janyo a kara yawan taimakaon tattalin arzikin da Masar take samu daga kungiyar Tarayyar Turai.