1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW
SiyasaLibiya

Libiya: Ko boyayyun gidajen yari nawa ne?

Mahmud Yaya Azare LMJ
May 22, 2025

An bankado gidajen yari dankare da mutanen da ake zaton sun mutu tsawon shekaru a Libiya wasunsu na karkashin kasa ne, inda tuni aka fitar da tsammanin samun mutanen da ke kulle a cikinsu da rai.

Libiya | Firaminista | Abdul Hamid Dbeibeh
Firaministan Libiya Abdul Hamid DbeibehHoto: Libyan Government of National Accord/AA/picture alliance

Kimanin gidajen yari shida aka gano, wadanda a ka yi amannar cewa mayakan sa-kai na rundunar Tabbatar da Zaman Lafiya ta kasar Libiyan wato Stabilisation Support Apparatus (SSA) da aka kashe jagoranta Abdel Ghani al-Kikli ne ke gudanar da su. An dai samu kimanin gawarwaki 58 da ba a gane ko su wanene ba a gidajen yarin, a yayin da aka balle su tare da sakin mutanen da ke cikinsu da aka jima da ba da sanarwar mutuwarsu ba tare da sanin sun tsare a cikin irin wadannan gidajen yarin ba.

Da ma ksar ta Libiya ta dade da tarwatsewa sakamkon rikiciHoto: Reuters/I. Zitouny

An dai kashe Abdel Ghani al-Kikli a wani dauki-ba-dadi da mayakansa suka yi da dakarun da ke kare gwamnatin hadin kan kasa karkashin jagorancin Firaminista Abdul Hamid Dbeibeh da al'ummomin kasa da kasa suka amince da ita. Musayar wutar ya afku ne, bayan da firaministan ya nemi al-Kikly ya mika ikon sansanonin da ke karkashinsa ga dakarun gwamnatin. Masu lura da abun da ke wakana a Libiya dai, sun yi ammanar cewa gidajen yarin da aka bankado somin tabi ne ta la'akari da yadda kasar ta Libiya ta zama sansanin kungiyoyin mayakan da ke samun tallafi da goyan baya daga 'yan siyasa da masu fasa kwabrin miyagun kwayoyi da fataucin dan Adam da suka fi karfin gwamnatin da ke fama da rarrabuwar kawuna.