1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW
SiyasaAfirka

Garkuwa da mutane: Sojojin Najeriya sun bai wa jama'a laifi

March 26, 2024

Babban hafsan tsaro a Najeriya, Janar Christopher Musa ya ce daga cikin matsalolin da ke hana su galaba a yaki da sace mutane shi ne gurbatattun bayanan sirri daga jama'a.

Hafsan tsaron Najeriya, Janar Christopher Musa
Hafsan tsaron Najeriya, Janar Christopher Musa da wasu jami'ai a AbujaHoto: KOLA SULAIMON/AFP

Hafsan hafsoshin Najeriya, Janar Christopher Musa ya ce ayyuka sun yi wa sojojin Najeriya yawa, abin kuma da ke sanya su dogaro da bayanan na sirii da suke samu daga fararen hula.

Babban hafsan tsaron, Janar Chris Musa, ya bayyana takaicin yadda jama'a ke kwatanta wa sojojin maboyar 'yan bindigar, amma kuma bayanan nasu ke hannu riga da asalin wuraren da suke kasancewa a zahiri.

A ranar Lahadin da ta gabata ne dai rundunar soji a Najeriyar, ta sanar da nasarar ceto daliban makarantar Kuriga su 137 wadanda 'yan bindiga suka sace a jihar Kaduna da ke arewacion kasar.

Ya kuma tabbatar da cewa an gwabza a tsakanin sojojin da 'yan bindigar da suka sace dalibai, kafin aka kai ga kubutar da su, sai dai bai yi bayanin yadda aka samo yaran ba tare da wani ain ya sami ko da daya daga cikin su ba.