Sake bude mashigar Rafah zai taimaki Gaza?
February 2, 2026
To sai dai irin sharuddan da Isra'ilan ta sanya kafin bude mashigar, ka iya janyo tarnaki ga ayyukan shige da fice na mutane a Zirin na Gaza, inda rahotanni daga kan iyakar ta Rafah ke nuni da cewa ba a tantance ko mutum daya ba balle mutane su fita har zuwa tsakiyar ranar Litinin biyu ga watan Fabarairun 2026 da aka fara amfani da damar bude ta.
Zaman jiran kila wa kala
Duk da cewa an cimma yarjejeniyar tsagaita wuta a Gaza har yanzu Isra’ila na ci gaba da kai farmaki, inda rahotanni ke nuni da cewa daga watan Oktobar bara kawo yanzu mutane 509 ne suka halaka yayin da wasu sama da 1,400 suka jikkata. A cewar ma’aikatar lafiya ta yankin, majinyata 20,000 ne ke jiran shiga Masar domin neman magani, yayin da 440 ke cikin halin rai-kwakwai mutu-kwakwai kana akwai masu cutarsankara wato cancer 4,000 da yara kanana 4,500.
Kungiyar Bayar da Agaji ta Red Cross ta nunar da cewa, babu dalilin kirkirar sabon bincike kan majinyatan da ke shirin fita bayan tuntuni jami'an lafiya da na tsaron sun gama tantanc esu. Wani magidanci da ke fama da cutar sankara wato cancer dansa kuma ke bukatar aikin cire alburusai a kwankwaso, ya nuna takaicinsa ga irin nawar da ake samu wajen ba su dammar ficewa.
Shin mazauna Gaza za su samu damar fita?
Dama dai kungiyar Hamas ta jima da nuna fargabarta kan cewa, Isra'ila za ta iya amfani da batun bude iyakar ta Rafah ba don sahalewa mazauna a Gaza ba sai dai domin ta wulakantasu da sake tursasa musu saboda ka da su yi sha'awar komawa idan suka samu damar fita. Tuni dai Masar ta ce, ta ware asibitoci 300 da likitoci 12,000 da za su tarbi dubban mazauna Gazan da ke shirin shiga kasar su yi jinya.