SiyasaAfirka
Ghana ta bukaci hadin kai don neman diyyar mulkin mallaka
November 14, 2023![Shugaban kasar Ghana Nana Akufo-Addo](https://static.dw.com/image/66881340_800.webp)
Talla
Wasu kasashen yamma dai a baya bayan nan sun amince cewa an aikata ba daidai ba kan abin da aka yi wa Afirka a lokacin mulkin mallaka kuma tuni gidajen adana tarihi na turai suka fara dawo wa da Afirka kayan tarihi da aka sace.
Karin Bayani: Jamus za ta mayar wa Najeriya da kayan tarihi
Shugaban na Ghana yana yawan magana kan biyan diyya inda ya yi amfani da jawabinsa a zauren babban taron Majalisar Dinkin Duniya wajen kira ga kasashen da suka yi wa Afirka mulkin mallaka su amsa girman tasirin abin da suka aikata na mulkin mallaka.