1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW
SiyasaAsiya

Girgizar kasa ta halaka mutane kusan dubu a Afghanistan

September 1, 2025

Adadin mutanen da suka mutu na ci gaba da karuwa cikin gaggawa, a yayinda wasu mutanen sama da 2800 suka samu raunuka.

Wasu yara a cikin buraguzan ginin a Nangarhar na Afghanistan
Wasu yara a cikin buraguzan ginin a Nangarhar na AfghanistanHoto: Aimal Zahi/Xinhua/dpa/picture alliance

Rahotannin daga birnin Kabul na cewa mutane sama da 800 suka mutu yayinda wasu da dama suka jikkata sakamakon mummunar girgizar kasa a gabashin Afghanistan, kamar yadda kafar yada labaran gwamnatin Taliban ta RTA ta rawaito.

Karin bayani: Afghanistan: Dusar kankara ta hallaka mutane 25

Ma'aikatar lafiya a Kabul da ke karkashin kulawar gwamnatin Taliban ta sanar da cewa har ya zuwa wannan lokaci suna ci gaba da tattara alkaluma tare kuma da zakulo mutanen da suka makale a baraguzai musamman a yankunan karkaka.

Karin bayani: Afghanistan: Gomman mutane sun mutu sakamakon ambaliyar ruwa

Ko a shekara ta 2015, wata mummunar girgizar kasa mai karfin maki 7.5 ta halaka mutane sama da 350 a kasashen Afghanistan da Pakistan.