1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Rashin tabbas a makomar gwamnatin Jamus

June 2, 2019

Shugabar jam'iyyar SPD a Jamus Andrea Nahles ta sanar a yau Lahadi cewa za ta sauka daga shugabancin jam'iyyar da kuma jagorancin rukunin yan jam'iyyar a majalisar dokoki bisa rashin goyon baya daga jam'iyarta

Andreas Nahles eine Neue -  SPD
Hoto: picture-alliance/dpa/U. Baumgarten

Nahles ta fuskanci matsin lamba sakamakon koma bayan da jam'iyyar ta samu da ke zama sakamako mafi muni a zaben majalisar dokokin Tarayyar Turai a makon da ya gabata.

Ta ce za ta ajiye mukamin shugabancin jam'iyyar ta SPD a gobe Litinin, yayin da a ranar Talata kuma za ta sauka daga shugabancin rukunin 'yan jam'iyyar a majalisar dokoki.

Murabus din na bazata ya sanya ayar tambaya akan makomar gwamnatin kawance ta Angela Merkel wadda dama take tangal-tangal. A yanzu dai Jam'iyar SPD ta Andrea Nahles, da kuma CDU ta Angela Merkel sune ke gudanar da gwamnatin kawance a Tarayyar Jamus, kuma idan har SPD ta janye daga kawancen, hakan na nufin gwamnatin Angela Merkel ta wargaje. 

Tsallake zuwa bangare na gaba Babban labarin DW

Babban labarin DW

Tsallake zuwa bangare na gaba Karin labarai daga DW