1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Cafke masu safarar mutane a Girka

Lateefa Mustapha Ja'afar
December 16, 2022

Wasu Turkawa hudu sun shiga hannun mahukuntan kasar Girka, sakamakon zarginsu da safarar bakin haure zuwa Turai.

Girka, Kythira | Aikin ceto | Kwale-kwale | Bakin Haure
Kwararar bakin haure zuwa Turai, ba bakon abu ba neHoto: Ippolytos Prekas/kythera.news/AP/picture alliance

Matakin na zuwa ne, bayan samun wani kwale-kwale makare da bakin haure kusan 100 da ya samu matsala a wani tsibiri da ke kusa da birnin Athens. Jami'an tsaron gabar teku, sun sanar da cewa mutanen hudu na cikin bakin hauren kusan 97 da aka samu cikin jirgin ruwan a Arewa maso Gabasahin Tsibirin Kea da ke yankin Kudu maso Arewacin gabar ruwan birnin Athens fadar gwamnatin kasar Girka.

 

Tsallake zuwa bangare na gaba Babban labarin DW

Babban labarin DW

Tsallake zuwa bangare na gaba Karin labarai daga DW