1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Gobara ta halaka majinyata Corona a Masar

Abdul-raheem Hassan
December 26, 2020

Mutane bakwai da ke jinyar cutar Corona sun mutu bayan da wuta ta tashi a asibitin da suke karbar jinya a birnin Alkahira na Masar. Sai dai ba a san me ya haddasa gobarar ba tukuna.

Ägypten Kairo | Coronavirus | Medizinische Mitarbeiter
Hoto: picture-alliance/Photoshot/A. Gomaa

Masu fama da cutar Corona akalla bakwai sun mutu a Masar sakamakon tashin gobara a asibitin da ake jinyan marasa lafiya a kusa da babban birnin Alkahira.

Hukumomin sun tabbatar da karin wasu mutane akalla biyar da gobarar ta jikkata, ba a gano musabbabin tashin gobarar a asibitin ba, amma jami'an kashe gobara sun shawo kan matsalar.

A watan Yuni, wasu majinyata sun mutu a wani asibitin shi ma inda gobara ta tashi yayin da wasu da dama suka jikkata.

Tsallake zuwa bangare na gaba Babban labarin DW

Babban labarin DW

Tsallake zuwa bangare na gaba Karin labarai daga DW