1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW
SiyasaAfirka

Gobara ta jikkata mutum 25 a Masar

October 2, 2023

Wata gagarumar gobara ta tashi a hedikwatar yan sanda a birnin Isma'iliya na kasar Masar inda akalla mutane 25 suka jikkata a cewar majiyoyin tsaro

Masar | Gobara a ofishin 'yan sanda a Ismailia
Masar | Gobara a ofishin 'yan sanda a Ismailia Hoto: AFP/Getty Images

Rahotanni sun ce ba a sami hasarar rayuka ba kuma an sami shawo kan gobarar.

Bakin hayaki ya turnuke ginin a yayin da gobarar ta tashi.

Kawo yanzu dai ba a san musababbin tashin gobarar ba.

Ana dai yawan samun tashin gobara a Masar inda ake da karancin fadakarwa kan tashin gobara da kuma jinkiri wajen kai agajin gaggawa.

A watan Augustan 2022 gobara ta hallaka mutane 41 a wani coci a birnin Alkahira inda aka rika kiran samar da ingantattun kayan aiki ga ma'aikatan kwana kwana.

 

Tsallake zuwa bangare na gaba Babban labarin DW

Babban labarin DW

Tsallake zuwa bangare na gaba Karin labarai daga DW