1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Gurbatacciyar allura ta hallaka yara a Juba

Yusuf Bala Nayaya
June 3, 2017

Yara goma sha biyar ne suka hallaka a Sudan ta Kudu sakamakon yi musu allurar kyanda wacce ta riga ta gurbata biyo bayan rashin ajiye ta cikin firji da ma amfani da sirinji guda wajan cakuda allurar.

Südsudan Medienreise Aktion Deutschland hilft
Hoto: Aktion Deutschland Hilft/Max Kupfer

Baya ga tabargazar da aka tabka wajen cakuda allurar akwai kuma wasu yara biyu tsakanin shekaru 12 zuwa 13 da aka samu cikin jami'ai masu allurar a cewar Riek Gai Kok da ke zama ministan lafiya a kasar ta Sudan ta Kudu.

A cewar Kok sakamakon bincike da suka gudanar ya gano jami'an da rashin bin ka'idoji na amfani da allurar rigakafin na kyanda a tsawon kwanaki hudu da aka yi ana wannan aiki da aka yi wa kimanin yara 300 allurar a jihar Kapoeta da ke yankin kudu maso gabashi na kasar.

Kaddamar da kamfen din dai na yaki da cutar kyanda a Sudan ta Kudu na zuwa ne bayan da aka samu yara 70 sun hallaka a kasar sakamakon barkewar cutar ta kyanda a wannan kasa da ke a yanayin yaki sama da shekaru uku.