1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Antonio Guterres ya ce akwai matsala a yakin Isra'ila a Gaza

November 9, 2023

Antonio Guterres ya ce tsananin hali na jinkai da kashe-kashen ake gani a Gaza sakamakon yaki ake ciki, na sanyaya gwiwar mutane a duniya dangane da yakin na Isra'ila a Zirin.

Sakatare Janar na MDD, Antonio Guterres
Sakatare Janar na MDD, Antonio GuterresHoto: Mark J. Sullivan/Zumapress/picture alliance

Sakatare Janar na Majalisar Dinkin Duniya, Antonio Guterres ya ce adadin rayuka da ke salwanta a Zirin Gaza na tabbatar da cewar akwai matsalar a yakin da Isra'ila ta kaddamar a yankin a kan kungiyar Hamas.

Cikin wata hirar da ya yi da kamfanin dillancin labarai na Reuters, Mr Guterres ya kuma ce kananan yaran da suka mutu a wannan rikici ya wuce kima.

A cewar jagoran na Majalsair Dinkin Duniya, hali na neman jinkai da ake gani a Zirin sakamakon halin da ake cikin na sanyaya gwiwar mutane a duniya dangane da yakin na Isra'ila a can.

Ma'aikatar lafiya ta yankin falasdinu dai ta ce sama da mutum dubu 10,500 ne suka mutu tun bayan tashin rikicin a ranar bakwai ga watan jiya.

A gefe guda kuma Antonio Guterres ya yi tir da garkuwar da kungiyar Hamas ta yi, da nufin hana afka mata.

Jakadan Isra'ila a Majalisar Dinkin Duniya Gilad Erdan, ya yi watsi da kalaman Mr. Guterres a game da yakin, yana mai cewa alkaluman da Hamas ke fitarwa na wadanda suka mutun, ba abu ne da za a yarda da su ba.