1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Guterres ya yi rantsuwar maye gurbin Ban Ki-moon

Yusuf Bala Nayaya
December 12, 2016

Antonio Guterres ya zama Babban Sakataren Majalisar Dinkin Duniya inda ya ke zama na tara a layi.

UN Generalversammlung - Antonio Guterres, Vereidigung als Generalsekretär in New York
Hoto: picture-alliance/dpa/J. Lane

Tsohon Firaministan Potugal Antonio Guterres  ya yi rantsuwar kama aiki a ranar Litinin din nan a matsayin Babban Sakataren Majalisar Dinkin Duniya inda ya ke zama na tara a layi, ya rattaba hannu kan wannan aiki gaban babban taron mai mambobi 193.

Guterres  mai shekaru 67 zai maye gurbin Ban Ki-moon mai shekaru 72 dan asalin Koriya ta Kudu daga ranar daya ga watan Janairu mai zuwa, abin da zai kawo karshen wa'adi biyu na shekara biyar-biyar da  Ban Ki-moon ya yi.

Guterres dai baya ga firaminista tsakanin shekarar 1995 zuwa 2002 ya rike kwamishina na Majalisar Dinmkin Duniyar kan 'yan gudun hijira tun daga shekarar 2005 zuwa 2015.

 

Tsallake zuwa bangare na gaba Babban labarin DW

Babban labarin DW

Tsallake zuwa bangare na gaba Karin labarai daga DW