SiyasaAfirka
Najeriya: Gwamnan Kano ya fita daga NNPP
January 23, 2026
Talla
Da yammmacin Jumma'ar 23 ga watan Janairun 2026 ne, wata tawaga karkashin mai maagana da yawun gwamnan na Kano Sunusi Bature Dawakin Tofa ta ziyarci mazabar Diso a karamar hukumar Gwale, inda nan ne mazabar gwamna Abba tare da mika takardar da ke kunshe da sakon gwamnan na ficewa daga jamiyyar. Wakilinmu a Kanon Nasir Salisu Zango ya ruwaito mai magana da yawun gwamnan na mai bayyana cewa, ficewar gwamnan tare da 'yan majalisun tarayya takwas da na jiha 20 da kuma shugabannin kananan hukumomi 44, ta biyo bayan rikici da ya dabaibaye NNPP din.