Gwamnati Burundi ta kauracewa taron zaman lafiya
October 25, 2018![Tanzania Arusha Friedensgespräche mit ehemaligem Präseidenten Bejamin Mkapa](https://static.dw.com/image/19277516_800.webp)
Sanarwar gwamnati ta bayar da dalilin kauracewa taron ganin ya zo daidai da ranakun da Burundi ke nuna alhinin kisan gillar da aka yi wa wasu tsofin shugabanin kasar a can baya. An shirya taron da kasar Tanzaniya ta dauki nauyinsa da zummar cimma daidaito a tsakanin bangaren gwamnati da jam'iyyar adawa, bayan da rikici a tsakaninsu ya ki ci-ya ki cinyewa, ana ganin yin hakan zai sa a sami hadin kai don tsara yadda za a tafiyar da babban zaben kasar na shekarra 2022.
Kawo yanzu dai, gwamanatin Burundi ta aki amincewa da bangaren adawa inda ta ayyana jam'iyyar a matsayin kungiya ta 'yan ta'adda. Wannan shi ne karo na biyar da ake zaman taron sulhunta rikicin kasar ta Burundi. Idan ba a manta ba, kasar ta tsunduma cikin rikicin siyasa a lokacin da shugaba Pierre Nkurunziza ya nemi yin tazarce a karo na uku, Rikicin da ya biyo bayan yunkurin ya lakume rayuka akalla dubu daya da dari biyu baya ga daruruwan da suka rasa matsuguninsu.